in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun tsara kundin mulkin Zimbabwe ta yi watsi da baiwa 'yan kasar izinin zabe a ketare
2018-05-31 10:28:27 cri
A jiya Laraba kotun tsara kundin mulkin kasar Zimbabwe ta zartar da hukuncin kin amincewa da baiwa 'yan kasar da suke zaune a kasashen waje izinin kada kuri'a a zaben kasar da za'a gudanar a ranar 30 ga watan Yulin wannan shekara.

Wannan hukunci na zuwa ne bayan da wasu 'yan kasar ta Zimbabwe dake zaune a kasashen waje wadanda kungiyar lauyoyi masu fafutukar kare hakkin dan adam 'yan asalin kasar ta Zimbabwe (ZLHR) ke wakilta, suka gabatar da bukatar a gaban kotu, inda suka yi ikirarin cewa, sabon kundin tsarin mulkin kasar da aka zartar a shekarar 2013 ya basu damar jefa kuri'a a lokacin da suke kasar waje.

To sai dai mataimakiyar babban mai shara'a ta kasar, Elizabeth Gwaunza, ta fada a lokacin zaman kotun cewa, babu wani muhimmanci dake tattare da wannan bukata.

Belinda Chinowawa na kungiyar lauyoyin ta ZHLR, yace wannan hukunci mummunan abin takaici ne.

A halin yanzu tsarin da Zimbabwe ke amfami da shi wajen zabe shi ne, duk wanda yake son jefa kuri'ar wajibi ne ya kasance yana zaune a cikin kasarsa, kuma zai kada kuri'ar ne a rumfunan zaben da aka tanada a kusa da inda yake zaune a duk fadin kasar. Kana an baiwa jami'an dake yiwa gwamnatin kasar aiki a wasu kasashen damar kada kuri'ar a yayin da suke ketare. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China