in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matasan ZANU-PF sun yi gangamin wayar da kai game da zabe cikin lumana
2018-06-07 13:12:12 cri
A jiya Laraba ne, daruruwan matasa magoya bayan jam'iyyar ZANU-PF mai mulki a Zimbabwe, suka gudanar da wani gangami na wayar da kan jama'a, game da muhimmancin gudanar da babban zaben kasar dake tafe cikin lumana. Hakan dai wani bangare ne na nuna goyon bayan su, ga takarar shugaba mai ci Emmerson Mnangagwa, wanda kuma ke yiwa jam'iyyar takara a zaben da za a kada a ranar 30 ga watan Yuli dake tafe.

Wannan ne dai karo na farko da kasar Zimbabwe za ta gudanar da babban zabe, ba tare da tsohon shugaban ta Robert Mugabe ba, wanda shi ne shugaba mafi dadewa da ya taba mulkar kasar. Kana shi ma tsohon mai hamayya da shi Morgan Tsvangirai ya rasu kafin wannan zabe na bana.

Tun kama aikin sa a watan Nuwambar shekarar da ta gabata, bayan murabus din shugaba Mugabe, Mr. Mnangagwa ya rika nanata bukatar daukacin jam'iyyun kasar su kasance masu bin doka da oda, tare da kauracewa tada husuma yayin zaben dake tafe. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China