in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanonin kasar Sin sun raba tallafin abincin bude baki a watan Ramadan a Cairo
2018-05-28 10:56:00 cri
Wasu kamfanonin kasar Sin sun aika da tallafin abinci domin baiwa masu karamin karfi don yin bude baki a gundumar Maadi dake birnin Cairo, domin taya al'ummar kasar Masar murna a cikin watan azumin Ramadan.

Kimanin akwatunan abinci 250 aka rarraba, kana mutane sama da 400 ne suka halarci bude bakin, a lokacin da al'ummar Musulmi ke bude bakin azumin watan Ramadan.

Ana sa ran raba akwatunan abinci kimanin 2,000, kana mutanen 5,000 ne ake fatan za su amfana da abincin bude bakin, wanda kamfanonin kasar Sin za su raba nan da kwanaki 15 masu zuwa a fadin kasar ta Masar, wanda ya hada da lardunan Cairo, Giza, Fayoum, Beni Suef da Aswan.

An shirya bada tallafin ne bisa hadin gwiwar ofishin jakadancin kasar Sin dake Masar da kuma majalisar kula da harkokin ciniki da masana'antu ta kasar Sin dake Masar, tare da hadin gwiwar kungiyar raya cigaban Masar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China