in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tsinci gawar bakin haure 6 kana an ceto wasu 82 a tekun Libya
2018-06-21 10:52:50 cri
Sojojin ruwan kasar Libya sun sanar a jiya Laraba cewa, sun yi nasarar ceto bakin haure 82 kana sun tsinci gawar mutum guda, yayin da tawagar jami'an bada agaji na Libyan Red Crescent suka gano gawar bakin hauren 5 a wurare daban daban a tekun kasar ta Libya.

Ayob Qassem, kakakin sojojin ruwan kasar Libya, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, dakarun tsaron tekun kasar sun ceto bakin haure kimanin 82 wadanda suka fito daga kasashen Afrika daban daban a wani samame da suka kaddamar na tsawon kilomita 48 a garin Garrabulli, mai nisan kilomita 55 daga Tripoli, babban birnin kasar.

Bakin hauren dai suna cikin wani karamin jirgin ruwa na roba ne. Sun shafe sa'o'i masu yawa suna jira a cikin tekun, kafin daga bisani dakarun tsaron tekun suka iso wajen inda kuma suka ceto su a karo biyu, in ji Qassem.

Kakakin sojojin ruwan ya tabbatar da cewa, an gano gawar mutumin da ya fada tekun bayan da jirgin ruwan ya tarwatse.

A kwanaki biyun da suka gabata ma, dakarun tsaron tekun Libyan sun ceto bakin haure kimanin 191 a lokuta daban daban, kana sun tsamo gawawakin mutane 11 wadanda suka nitse a tekun. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China