in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Alkawurran kasashen duniya na sake tsugunar da 'yan ci ranin Libya na tafiyar hawainiya
2018-06-20 09:25:03 cri
Shugaban hukumar kula da 'yan gudun hijira na MDD, Flippo Grandi, ya ce cika alkawurran da kasashen duniya suka dauka na sake tsugunar da 'yan ci rani dake Libya na tafiyar hawainiya.

Flippo Grandi, ya bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai da aka yi jiya a Tripoli babban birnin Libya, bayan ya ziyarci sansanonin da cibiyoyin ajiye 'yan ci rani.

Ya ce akwai bukatar gaggauta shirin sake tsugunarwar, yana mai cewa wani bangare na shirin ne kadai aka aiwatar, inda aka karbi kasa da 'yan ci rani 2,000.

Ya ce an tsugunar da wani adadi kalilan a Italiya da Romania. Kuma an kai kimanin 'yan ci rani 1,300 wanda shi ne adadi mafi yawa, zuwa Niger. Yana mai godewa Gwamnatin Niger bisa shirya wani wuri na wucin gadi na karbar 'yan ci ranin.

Jami'in ya kuma yi kira da a gaggauta mayar da 'yan gudun hijirar Libya zuwa biranensu, inda ya ce 'yan gudun hijirar na ci gaba da galabaita saboda rashin wata yarjejeniya a hukumance. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China