in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in kare hakkin dan adam na MDD ya ce janyewar Amurka daga kwamitin MDD abin takaici ne da mamaki
2018-06-20 10:56:29 cri
Babban jami'i mai kula da kwamitin kare hakkin dan adam na MDD Zeid Ra'ad Al Hussein ya bayyana a daren jiya Talata cewa, matakin da Amurka ta dauka na ficewa daga kwamitin kare hakkin dan adam na MDD abin takaici ne, kuma ya zo da ban mamaki.

Zeid ya ce, bisa halin da ake ciki a duniya a yanzu, kamata ya yi Amurka ta kara azama, maimakon ta ja da baya, Zeid ya furta hakan ne biyowa bayan matakin da Amurkar ta dauka na baya bayan nan na janyewa daga kwamitin kare hakkin dan adam na MDDr.

Haka zalika bayan sanarwar da Amurkar ta fitar na janyewarta, shugaban kwamitin kare hakkin dan adam na MDD Vojislav Suc ya nanata cewa, abu mafi muhimmanci shi ne a dauki kwararan matakai kuma kwamitin majalisar ya tsaya tsayin daka a wannan yanayin da ake ciki tare da hadin gwiwar gamayyar kasa da kasa domin tunkarar kalubalolin da tsarin kare hakkin dan adam ke fuskanta a kullum. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China