in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi maraba da matakan magance rikicin siyasar kasar Madagascar
2018-06-13 09:57:40 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi maraba da kafa sabuwar gwamnati a kasar Madagascar da ma sabon firaministan da aka nada kamar yadda babbar kotun kundin tsarin mulkin kasar ta yanke hukuncin yin haka.

Cikin wata sanarwar da ya fitar ta hannun kakakinsa Stephane Dujarric, Guterres ya kuma yabawa shugaba Henry Rajaonarimampianina da dukkan masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar kasar game da matsayar da suka cimma na kare muradun al'ummar kasar.

Jami'in na MDD ya kuma yi kira ga masu fada a ji a harkokin siyasar kasar, da su karfafa yin tattaunawa don kare irin ci gaban da aka samu a kokarin da ake na tabbatar da zaman lafiya da dorewa mulkin demokiradiya da ma ci gaban kasar baki daya.

Guterres ya kuma nanata kudurin MDD na ganin an gudanar da ingantattun zabukan kasar na wannan shekarar lami lafiya kamar yadda kudin tsarin mulkin kasar ya tanada. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China