in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNSMIL ya karyata rahoton dake cewa 'yan bindiga sun rufe ofishin MDDr a Libya
2018-05-28 11:38:36 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake Libya (UNSMIL) ya karyata rahotannin dake cewa 'yan bindiga sun rufe ofishin shirin MDDr dake helkwatarta a Tripoli babban birnin kasar.

Kakakin UNSMIL Sawsan Ghosha, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, rahotannin dake nuna cewar 'yan bindigar sun rufe helkwatarta ba gaskiya ba ne.

Kafafen yada labarai na cikin gidan kasar sun rawaito cewa wasu 'yan bindiga sun rufe helkwatar MDDr har ma sun hana jami'anta shiga ofisoshinsu.

Haka zalika, kafafen yada labaran sun wallafa wasu hotunan motocin 'yan bindigar da suka girke a kusa da helkwatar MDDr.

Helkwatar ta UNSMIL tana garin Janzour, wanda ke da tazarar kilomita 15 daga Tripoli babban birnin kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China