in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS ta dauki nauyin harin da aka kai kan wani shingen bincike a Libya
2018-06-03 16:05:40 cri
Kungiyar IS, ta dauki alhakin harin da aka kai kan wani shingen bincike, jiya Asabar, a kudancin birnin Ajdabiya dake gabashin Libya, al'amarin da ya raunata wata mata da wasu mutane 5.

Wata sanarwa da kafar yada labaran kungiyar IS ta A'maq ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce, wasu sojojin daular sun kai samame da makamai daban-daban, kan wani ofishin 'yan sanda da sanyin safiyar jiya a yankin Al-Gannan dake kudancin Ajadabiya, inda suka yi bata kashi da dakarun Janar Haftar.

'sojojin daula' ita ce kalmar da kungiyar IS ke amfani da ita wajen kiran mayakanta da suka kai harin ta'addanci.

Hukumar tsaron Ajadabiya, ba ta bayyana adadin wadanda harin ya rutsa da su daga cikin jami'anta ba. Amma kungiyar IS, ta tabbatar da cewa, an kashe wani adadi na jami'an tsaro tare da kona motoci yayin harin. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China