in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta ce masu shiga tsakani na kasa da kasa kan nukiliyar Iran sun tsame Amurka
2018-05-28 11:01:52 cri
Ministan harkokin wajen kasar Iran Mohammad Javad Zarif ya bayyana cewa masu shiga tsakani na kasa da kasa game da batun nukiliyar kasar Iran sun sake tsame Amurka daga cikin yarjejeniyar nukiliyar ta Iran.

Kasashen duniya sun nuna goyon bayansu ga yarjejeniyar nukiliyar ta Iran, in ban da Irsra'ila da wasu tsirarun kasashen Larabawa inda suka goyi bayan Amurka, yarjejeniyar wacce aka fi sani da (JCPOA).

An jiyo Zarif yana jawabi ta gidan talabijin din kasar yana cewa, sun yi amanna har yanzu kasa da kasa suna goyon bayan yarjejeniyar ta JCPOA, sai dai shugaban kasar Amurka Donald Trump bai sauya matsayinsa game da sharrudan da ya gindaya ba.

Ya nanata cewa, sun yi amanna da kasarsu, kuma hakan shi ne ke baiwa kasarsu kwarin gwiwa a matsanancin halin da ake ciki game da warware takaddamar shirin nukiliyar ta Iran. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China