in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya za ta taimaka wajen shigar da mayakan Boko Haram da suka tuba cikin al'umma
2018-06-09 14:55:11 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce ta kammala shirye-shiryen wayar da kan al'ummomin a yankin arewa maso gabashin kasar dake fama da rikicin 'yan tada kayar baya, domin su karbi mayakan Boko Haram da suka tuba, suka ajiye makamai.

Daraktan hukumar wayar da kai ta kasar (NOA) Musa Shantu, ya bayyana jiya a Abuja babban birnin kasar cewa, za a gudanar da shirin ne a yankunan Maiduguri da Goza na jihar Borno.

Ya ce wayar da kan ya zama wajibi duba da yadda wadanda suka tuba, kuma suka shiga shirin gyaran hali, kana suka shirya komawa cikin al'ummominsu ke fuskantar kalubale.

Musa Shantu, ya ce komawa cikin al'umma ya zama abu mai wahala ga galibinsu, la'akari da yadda al'ummomin ke da mummunan tunani kansu.

A cewarsa, hukumar NOA za ta tattauna da jama'a domin tabbatar musu cewa mayakan da suka tuba, sun canza tare da sauya hali. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China