in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun sace matafiya a kalla 23 a arewacin Nijeriya
2018-06-09 15:11:00 cri
Matafiya a kalla 23 ne aka sace jiya Jumma'a a jihar Kaduna dake yankin arewa maso yammacin Nijeriya.

Kafar yada labarai ta PR Nijeriya, wadda ke shirya sanarwa ga hukumomin tsaro, ta ruwaito cewa, daga cikin wadanda aka sace akwai wata mace da jaririyarta.

Matafiyan na tafiya ne a kan titin nan mai hadari na Birnin-Gwari dake Kaduna, a lokacin da 'yan bindigar suka tsaida su a kwanar-tsauni, dake tsakanin kauyukan Udawa da Labi dake yankin.

Wani direban motar haya da al'amarin ya auku kan idonsa mai suna Mohammed Kebi, ya ce a kalla motoci 5 masu satar mutanen suka tsare da misalin karfe 11 na safiyar jiya Jumma'a.

Shi ma wani ganau Musa Yakubu, ya ce titin na Birnin-Gwari ya zama inda masu satar mutane don neman kudin fansa ke cin karensu ba-babbaka.

Tun daga farkon shekarar nan, an samu gomman hare-hare a yankin na arewa maso yammacin Nijeriya, duk da kokarin da gwamanatin kasar ke yi na ganin ta kawo karshen al'amarin. (Fa'iza Msuatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China