in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nuna damuwa ga harin sama da aka kai a jihar Idlib ta kasar Syria
2018-06-11 14:08:16 cri
Babban sakataren MDD António Guterres ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa a ranar 10 ga wata, inda ya nuna damuwa ga harin sama da aka kai a garin Zardana dake jihar Idlib ta kasar Syria a ranar 7 da 8 ga wannan wata wadanda suka haddasa mutuwa da raunata mutane masu yawa.

Guterres ya yi kira da a gudanar da bincike kan harin, musamman ga batun sake kai harin yayin da masu aikin ceto suke gudanar da aikinsu a wurin.

Guterres ya bayyana cewa, jihar Idlib "yankin rage rikice-rikice" ne da aka kafa bisa yarjejeniyar da bangarori daban daban suka cimma, kana ya yi kira ga bangarorin da abin ya shafa da su cika alkawuransu. Ya jaddada cewa, mutane kimanin miliyan 2 da dubu 300 a jihar Idlib suna fuskantar hadari, ciki har da kashi 60 bisa 100 daga cikinsu sun je wajen ne daga sauran yankunan kasar a sakamakon rikice-rikice. Guterres ya yi kira ga bangarorin da rikicin ya shafa da su daina nuna kiyayya, da kalubalantar bangarori da abin ya shafa da su tabbatar da tsaron fararen hula da ayyukan more rayuwa masu amfanin jama'a bisa dokokin jin kai na kasa da kasa. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China