Kafar talabijin ta kasar ta ce, kwace yankin ya biyo bayan wata guda da sojojin suka kwashe suna bata kashi da mayakan, inda suka yi nasarar sake kwato wani yanki dake karkashin ikon mayakan na IS.
Tun da sanyin safiyar yau, gidan talabijin na kasar, ya ce an dakatar da tsagaita bude wuta da tsakar ranar jiya zuwa yau Litinin, domin a kwashe masu bukatar agaji daga yankin na Hajar al-Aswad kafin sojojin su ci gaba da daukar matakai a yankin. (Ibrahim)