in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Daidaita batun Syria a siyasance zabi ne daya kacal, in ji manzon musamman na kasar Sin
2018-04-26 10:42:04 cri
Manzon musamman na gwamnatin kasar Sin kan batun Syria Mr. Xie Xiaoyan wanda ke halartar taron kasa da kasa kan batun Syria a birnin Brussels, a jiya Laraba ya jaddada cewa, matakan soja ba za su taimaka ga daidaita batun Syria ba, kuma matakan siyasa su ne zabi daya kacal da ya dace a bi.

A jawabin da ya gabatar a gun taron, Mr. Xie Xiaoyan ya gabatar da shawarwari guda uku, wato na farko a tsaya ga yin shawarwari, na biyu kuma a tabbatar da tsagaita bude wuta, na uku, ya kamata kasa da kasa su hada karfinsu a kan batun.

Mr.Xie Xiaoyan ya kuma kara da cewa, sau da dama kasar Sin ta samar da gudummawar kayayyaki, da kudi cikin gaggawa ga al'ummar Syria, ciki har da 'yan gudun hijira da ke kasashen ketare, gudummawar da kawo yanzu ta kai kudin Sin yuan miliyan 740. A gaba, kasar Sin za ta gaggauta cika alkawuranta na samar da agajin jin kai, za ta kuma karfafa gwiwar kamfanonin kasar, ta yadda za su shiga aikin farfado da Syria muddin dai za a iya tabbatar da tsaronsu.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China