in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya fara ziyarar kwanaki biyu a kasar Morocco
2018-06-11 08:51:44 cri
A jiya Lahadi ne, shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya isa kasar Morocco don fara ziyarar aiki ta kwanaki biyu. Sarki Mohammed na 6 da yarima Moulay El Hassan da firaministan kasar Saadeddine El Othmani da mambobin majalisar zartarwar kasar ne suka tarbe shi a filin jiragen sama na Rabar-Sale dake kasar.

A yayin ziyararsa a kasar ta Morocco, ana sa ran shugaba Buhari ya tattauna da sarki Mohammed na 6, sannan su jagoranci bikin sanya hannu kan wasu jerin yarjejeniyoyi, kamar yadda wata sanarwa da mahukuntan kasar suka fitar.

Dangantaka tsakanin Najeriya da Morocco dai ta ci gaba da bunkasa a 'yan shekarun da suka gabata. Koda a ziyarar da sarkin na Morocco ya kai Najeriya a watan Disamban shekarar 2016, kasashen biyu sun sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi, tare da cimma matsaya game da hadin gwiwa a aikin shimfida bututun iskar gas, matakin da zai kai ga hade kasashen arewaci da yammacin nahiyar Afirka da kuma baiwa shiyyar damar cin gajiyar makamashi na kashin kanta, da hanzarta aiwatar da ayyukan samar da wutar lantaki da bunkasa muhimman ayyukan da suka shafi harkokin tattalin arziki da masana'antu. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China