in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da dandalin tattaunawa kan karfafa zumunci tsakanin Sin da Morocco a Agadir
2018-03-28 13:09:25 cri
An gudanar da dandalin tattaunawa game da inganta zumunta tsakanin kasashen Sin da Morocco karo na biyu a birnin Agadir dake kudancin kasar Morocco. Taron dai ya gudana ne tsakanin ranekun 26 zuwa 27 ga watan nan.

Dandalin, wanda kungiyar sada zumunta tsakanin jama'ar kasar Sin da kasashen waje ta Sin ta shirya, gami da hadin gwiwar kungiyar mu'amalar sada zumunci tsakanin Morocco da Sin na da taken 'Morocco, mashigar shawarar ziri daya da hanya daya ta kasar Sin a nahiyar Afirka.'

Mataimakiyar shugaban kungiyar sada zumunta tsakanin jama'ar kasar Sin da kasashen waje ta Sin, Lin Yi, ta ce, akwai dadadden zumunci tsakanin Sin da Morocco, kana, a matsayin membar kungiyar tarayyar Afirka, da ta kawancen kasashen Larabawa, Morocco za ta iya kara taka muhimmiyar rawa a fannoni da dama, ciki har da fadada hadin-gwiwa, da raya kyakkyawar hulda tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka da kasashen Larabawa, musamman ma wajen aiwatar da shawarar 'ziri daya da hanya daya'.

An kafa dandalin tattaunawa don karfafa zumunci tsakanin Sin da Morocco ne da nufin kara samun fahimtar juna tsakanin birane da jihohin kasashen biyu, da inganta hadin-gwiwarsu a fannonin kasuwanci da al'adu, da kuma yawon shakatawa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China