in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco da MDD sun tattauna game da yadda za'a inganta tsaron jami'an kiyaye zaman lafiya a Afrika
2018-02-13 11:19:17 cri
Ministan kasar Morocco mai kula da sha'anin tsaron kasa da jami'in shirin wanzar da zaman lafiya na MDD sun tattauna game da yadda za'a inganta yanayin tsaron dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD dake Afrika.

Abdeltif Loudyi, ministan kasar Morocco, da laftanal janar Carlos Humberto Loitey, mai bada shawara kan harkokin soji na shirin wanzar da zaman lafiya na MDD, sun kuma tattauna game da irin gudunmowar da Moroccon ke baiwa shirin na MDD.

Jami'an biyu, sun nazarci matakan da za'a bi wajen inganta shirin wanzar da zaman lafiyar na MDDr.

Game da wannan batu, Loudyi ya jaddada irin kokarin da masarautar Moroccon ke yi wajen samun nasarar shirin kiyayen zaman lafiya, kana ya yabawa sabbin dabarun da babban magatakardar MDD Antonio Guterres ya bullo da su, a matsayin wasu sauye-sauye da za su taimakwa shirin kiyaye zaman lafiyar na MDDr.

Haka zalika, Loitey, ya jaddada ta'aziyya ga masarautar bisa rasuwar wasu jami'ai masu wanzar da zaman lafiyar 'yan kasar Morocco a lokacin da suke bakin aiki, bisa irin jarumtar da suka nuna a wajen aikin kiyaye zaman lafiya a jamhuriyar tsakiyar Afrika.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China