in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco ta katse huldar diflomasiya da kasar Iran
2018-05-02 09:14:30 cri
Kasar Morocco ta sanar da katse huldar diflomasiya da kasar Iran, 'yan shekaru bayan dowa da hulda a tsakaninsu.

Da yake karin haske kan hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, ministan harkokin wajen kasar Morocco Nasser Bourita, ya ce kasarsa za ta kori jakadan kasar Iran dake Morocco sannan ta rufe ofishin jakadancinta dake Tehran, saboda yadda Iran din take goyon bayan kungiyar 'yan awaren Polisario dake yammacin Sahara.

Ministan ya ce, kasarsa tana da kwararan shaidu game da hannun kasar Iran ta abokanta Hezbollah dake kasar Lebanon, inda take goyon bayan sojojin Polisario ta yadda take horos da mambobin kungiyar domin ta kawo illa ga tsaro da zaman lafiyar Morocco.

Bourita ya ce, tuni ya mikawa takwaransa na kasar Iran wadannan shaidu, wadanda suka hada da muhimman takardu kan yadda aka mikawa kungiyar 'yan tawayen makamai. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China