in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya shirya liyafar maraba ga bakin dake halartar taron SCO
2018-06-09 20:29:26 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya shirya liyafar cin abincin dare a yau Asabar, domin yin maraba ga bakin da suka hallara a birnin Qindao domin taron koli na kungiyar hadin kai ta Shanghai wato SCO.

Da yake gabatar da jawabi, Xi Jinping, ya ce yana farin cikin ganinsu a birnin Qingdao na lardin Shandong dake gabar rawayan teku.

Ya kara da cewa, a madadinsa da gwamnati da al'ummar kasar Sin, yana yi wa dukkansu maraba, musammam Shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da suka halarci taron majalisar shugabannin kasashe mambabin SCO. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China