Ofishin OCHA ya kuma ce, ambaliyar ruwa ta yiwa dubban jama'a da ma kayayyakin more rayuwa barna, baya ga wadanda suka rasa mutsugunansu.
Mahaukaciyar guguwar mai tafe ruwan sama ta haifar da mummunan yanayin jin kai a jihohin Somaliland da Puntland da ma wasu yankunan da ake takaddama a kansu, inda suka fuskanci fari a shekarar 2015.
Rahotanni daga yankin na cewa, kwale-kwalen kamu kifi da dama sun bace a yankin. Koda yake masana hasashen yanayi na cewa, karfin mahaukaciyar guguwar yana raguwa., inda yanzu ta doshe wasu sassan Habasa, Djibouti da arewa maso yammacin Somaliland.(Ibrahim)