Shugaban kasar Somaliya Mohamed Abdullahi Mohamed ya bayar da wata sanarwa a daren ranar 1 ga wata, inda ya bayyana cewa, mutane kimanin dubu 500 ne ke fama da ambaliyar ruwa a kasar a kwanakin nan, ciki har da mutane dubu 175 da suka rasa matsugunansu.
Shugaba Mohamed ya kara da cewa, gwamnatin kasar Somaliya na daukar matakai don tinkarar matsalar jin kai sakamakon abkuwar ambaliyar ruwan. Ya kuma yi kira ga kasashen duniya da su samar da taimako ga kasarsa. Ya zuwa yanzu gwamnatin kasar ta kafa kwamitin tinkarar matsalar domin taimakawa jama'a dake fama da bala'in. (Kande Gao)