Mataimakin kakakin hukumar ta OCHA Jens Laerke, ya bayyanawa zaman MDD cewa, ambaliyar ta shafi mutane 718,000 a yankin arewa maso gabashin Afirka,yayin da mutane 132 suka mutu a Kenya.
Laerke ya ce, abokan hulda masu gudanar da ayyukan jin kai da hukumomi Somali suna samar da kayayyakin taimakon rai, taimakon na'urorin sauko da mutane zuwa kasa, da raba buhunan kasa don gyara gabobin kogin da suka lalace. Haka kuma, ana tsammanin ci gaba da fuskantar ambaliyar ruwa a wasu yankuna a kasar Habasha.
A watan Afrilu kadai, kimanin mutane 171,000 ne suka rasa matsugunansu a sassan kasar, galibi saboda ambaliyar da ta faru a yankin Somali.(Ibrahim)