Mataimakin shugaban ICRC a Somaliya Daniel O'Malley, ya bayyana cewa, wasu mutane dauke da makamai ne suka kutsa kai cikin harabar ofishin na ICRC da misalin karfe 8 na daren ranar Laraba, inda kuma nan take suka yi awon gaba da wata jami'ar jinya 'yar kasar Jamus.
Mahukuntan ICRC dai sun ce suna tuntubar sassa masu ruwa da tsaki daban daban, a wani mataki na kokarin ceto wannan jami'a. Sai dai sun ce ba za su yi karin haske, game da halin da ake ciki ba game da kokarin da suke yi na ceto ta.