in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadar White House ta ce ganawar Shugaba Trump da Kim Jong Un za ta gudana da misalin karfe 9 na safiyar ranar 12 ga wata
2018-06-05 09:52:02 cri

Fadar White House ta ce an shirya gudanar da taro tsakanin Shugaban Amurka, Donald Trump da shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un, da misalin karfe 9 na safiyar ranar 12 ga watan nan, a Singapore.

Yayin wani taron manema labarai, kakakin fadar White House Sarah Sanders, ta ce tuni ayarin masu shirya ziyarar shugaban kasar suka isa Singapore, inda suke kokarin kammala duk wani shirye-shirye, kana za su kasance a can har sai an fara taron.

Da take bayanna cewa bangaren Amurka na shiryawa taron yadda ya kamata, ta ce ayarin Amurka dake iyakar da aka shata tsakanin kasashen Koriya 2, na ci gaba da tattaunawar diflomasiyya da ayarin Koriya ta arewa.

Ta kara da cewa, ana samun kyawawan sakamako da nasarori game da tattaunawar.

Bayan ganawarsa da Kim Yong Chol, wanda ya kai masa wasikar da shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un ya aike masa, Shugaba Trump ya bayyana a ranar Jumma'ar da ta gabata cewa, zai gana da shugaban na Koriya ta arewa a ranar 12 ga watan nan a Singapore kamar yadda aka tsara tun farko. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China