in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan ganin za a samu nasara a shawarwarin shugabannin Koriya ta arewa da Amurka
2018-05-23 20:17:55 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Lu Kang ya ce, kasarsa na fatan za a yi ganawa tsakanin shugabannin kasashen Koriya ta arewa da Amurka yadda ya kamata, za kuma a samu sakamako mai yakini.

Lu ya bayyana haka ne a yayin manema labaru da aka shirya a yau Laraba a nan birnin Beijing, inda ya kara da cewa, yanzu an samu dama mai kyau wajen warware matsalar zirin Koriya a siyasanci, kuma kasar Sin na fatan bangarori daban daban, musamman ma Amurka da Koriya ta arewa za su yi amfani da wannan damar don warware sabanin dake tsakaninsu kan wannan batu. Baya ga haka, Lu ya ce, Sin za ta ci gaba da taka rawa kan wannan batun.

Rahotani na cewa, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana a jiya Talata cewa, mai yiwuwa ne za a samu jinkiri game da ganawar da za su tsakaninsa da takwaransa na kasar Koriya ta arewa Kim Jong Un. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China