in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: Kiyaye yarjejeniyar kasa da kasa hakkin tushe ne bisa dokokin kasa da kasa
2018-06-02 16:24:49 cri
Memban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kiyaye yarjejeniyar tsakanin bangarori 2, muhimmin hakki ne bisa dokokin kasa da kasa, kuma ya kamata manyan kasashe su tabbatar da hakan domin nunawa sauran kasashe yadda ake yi, maimakon sabawa.

Wang Yi ya ce kasar Sin za ta sanya kokari tare da kungiyar EU wajen tabbatar da yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran a dukkan fannoni.

Wang Yi ya kuma amsa tambayoyi tare da wakiliyar kungiyar EU Federica Mogherin game da batun nukiliyar kasar Iran, inda ya bayyana cewa, ya kamata a yi shawarwari cikin adalci, da tattauna sauyin yanayin da ake ciki da sabbin matsalolin da ake son lura da su tare, bisa yanayin ci gaba da tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar batun nukiliyar Iran a dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China