in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista:Kasar Ghana za ta hukunta masu aikata ba dai-dai ba yayin gudanar da ayyukan samar da zaman lafiya
2018-05-30 09:51:52 cri
Ministar harkokin waje da hadin gwiwar yunkuna ta kasar Ghana Shirley Ayorko Botchwey ta ce, kasarta tana matukar nazartar batun yiwa mata lalata da cin zarafi da ake aikatawa a ayyukan wanzar da zaman lafiya na MDD da matukar muhimmanci.

Ministar wadda ta bayyana hakan yayin da take jawabi a bikin kafa tuta da aza furanni, don tunawa da ranar ma'aikatan wanzar da zaman lafiya ta kasa da kasa ta MDD da ya gudana a birnin Accrar kasar Ghana, ta ce a matsayinsa na mamba na rukunin hadiman babban sakataren MDD dake yaki da yin latata da cin zarafi yayin ayyukan wanzar da zaman lafiya, shugaba Nana Addo Dankwa Akufo-Addo na kasar Ghana ya bayyana karara cewa, zai taimakawa waje magance wannan mummunar ta'ada.

Don haka ta ce, gwamnati za ta dauki kwararan matakai kan duk wani mai kayan sarki ko farar hula da aka tabbatar ya aikata ba dai-dai ba yayin da yake gudanar da aikinsa na tabbatar da zaman lafiya, sabanin halayen kwarai da dakarun kasar ta Ghana dake ayyukan wanzar da zaman lafiya na MDD suka nuna a shekarun baya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China