in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin kunar bakin wake ya yi sanadin mutuwar mutane 4 a Nijeriya
2018-05-29 09:43:04 cri
Rundunar 'yan sandan jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 4, sanadiyyar wani harin kunar bakin wake da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram da kai wa garin Konduga na jihar.

Kwamishinan 'yan sandan jihar, Damian Chukwu, ya ce wasu mutane 7 kuma sun jikkata a harin da aka kai da daren ranar Lahadi.

Damian Chukwu, ya shaidawa manema labarai cewa, maharan sun samu shiga garin ne domin kaddamar da harin ta kauyen Mashimari, dake yankin, ta kusa da wani sansanin 'yan gudun hijira.

Konduga mai yawan jama'ar da suka kai 13,000, ya sha fuskantar hare-haren Boko Haram. Kuma galibin mazauna kauyen sun kasance manoma.

Tun daga shekarar 2009, kungiyar Boko Haram ta yi sanadin mutuwar mutane sama da 20,000 tare da raba wasu miliyan 2.3 da matsugunansu a Nijeriya. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China