in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 42 a arewa maso yammacin Najeriya
2018-05-24 09:39:21 cri
Kungiyar direbobin mota ta kasa a Najeriya (NURTW) ta sanar da cewa, wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi garkuwa da fasinjoji 42 yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa jahar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya a cikin sa'o'i 24 da suka gaba.

Wani babban jami'in kungiyar NURTW ya shedawa 'yan jaridu a Abuja, babban birnin kasar cewa, lamarin ya faru ne tsakanin yammacin ranar Talata zuwa safiyar jiya Laraba.

An samu cikakken rahoton faruwar lamarin ne sa'o'i 24 bayan da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da matar wani kwamishina mai ci a jahar Zamfara dake arewa maso yammacin kasar tare da wasu mutane 6.

Shugaban wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya bayyana cewa, wasu daga cikin direbobin motar da suka tsallake rijiya da baya daga hannun masu garkuwar, sun tabbatarwa 'ya'yan kungiyar yadda lamarin ya faru.

Majiyar ta tabbatar da cewa, mafi yawan fasinjojin da suka hada da mata da kananan yara suna kan hanyarsu ta zuwa Kano ne a lokacin da lamarin ya faru.

Kazamin aikin da masu dauke da makaman suka kaddamar a kwanan nan a kan babbar hanyar Birnin-Gwari zuwa Kaduna inda suka yi garkuwa da fasinjoji 107, ya sa babban hafsan sojojin Najeriya, laftanar janar Tukur Yusuf Buratai, ya baiwa dakarun sojin kasar umarnin su kawo karshe kashe kashe da barnata dokokin jama'a da aka samu a makonni ukun da suka gabata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China