in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta ja hankalin magoya bayan ta gabanin bude gasar cin kofin kwallon kafa FIFA da za a buga a Rasha
2018-05-22 09:38:12 cri
Ministan ma'aikatar wasanni da matasa a tarayyar Najeriya Solomon Dalung, ya ja hankalin 'yan kasar da su yi taka tsantsan, game da masu yi musu robon baka, na cewa za su sama masu damar bin tawagar magoya bayan kungiyar kwallon kafar kasar zuwa Rasha, inda nan da 'yan makwanni, za a fara buga gasar cin kofin duniya da hukumar FIFA ke shiryawa.

Solomon Dalung ya ce akwai wasu mutane da ke yaudarar al'umma ta wannan hanya, suna musu alkawuran karya, don haka ya zama wajibi 'yan kasar su kaucewa fadawa hannu irin wadannan bata gari.

Kalaman ministan na zuwa ne bayan da shugaban kasar Muhammadu Buhari, ya yi tsokaci game da shirin da kungiyar Super Eagles ta Najeriya ke yi na tafiya, domin buga gasar cin kofin duniyar cikin nasara.

Ya ce "labarai na zuwa gare mu cewa, ana ta yin wasu abubuwa nan da can, wadanda ke da alaka da yaudarar jama'a, don haka ga masu son zuwa kallo ko goyon bayan tawagar kasar mu ya dace su yi a hankali".

Daga nan sai ministan ya yi kira ga fadar shugaban Najeriyar da ta hanzarta amincewa da kasafin da ake bukata domin cimma nasarar shirye shiryen da kungiyar ta Super Eagles ke yi na halartar gasar ta Rasha. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China