Shugaban hukumar bada agajin gaggawa na jahar Katsina Aminu Waziri, ya bayyana cewa, kimanin gidaje 500 ne iskar ta lalata da yammacin ranar Alhamis.
Waziri, ya kara da cewa, wani barikin soji da sansanin sojojin sama dake kwaryar birnin Katsinan na daga cikin wuraren da iftila'in ya shafa.
Hukumar mulkin karamar hukumar ta Katsina ya bayyana lamarin da cewa iftila'i ne daga Allah wanda dan adam bai isa ya hana faruwarsa ba, ya ce tuni aka tura jami'ai zuwa yankin domin su duba adadin barnar da iskar ta haddasa, da nufin samar da kayayyakin tallafi ga wadanda bala'in ya shafa. (Ahmad Fagam)