in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Sojoji sun ceto mutane 53 daga hannun mayakan Boko Haram
2018-05-17 20:33:55 cri
Kakakin rundunar sojojin Najeriya Onyema Nwachukwu, ya ce dakarun rundunar sun samu nasarar ceto wasu mutane 53, wadanda mayakan kungiyar 'yan ta'adda ta Boko Haram ke tsare da su a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Onyema Nwachukwu ya ce cikin wadanda aka kubutar din, akwai mata 33 da yara kanana 16, sai kuma maza guda 4. Hakan dai a cewar jami'in ya biyo bayan wani sumame ne da sojojin suka gudanar a ranar Talata.

Jami'in ya kara da cewa, tuni sojoji suka fara aikin tantance wadanda aka kubutar kafin mika su ga mahukuntan jihar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China