in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan wadanda harin IS ya hallaka a Libya ya kai mutum 14
2018-05-02 20:56:25 cri

Rahotanni daga kasar Libya na cewa, yawan mutanen da harin kunar bakin wake ya hallaka, a harabar hukumar zaben kasar dake birnin Tripoli ya kai mutum 14 baya ga wasu mutum sama da 10 da suka ji raunuka.

Wasu 'yan kunar bakin wake ne dai suka kutsa kai cikin harabar hukumar zaben kasar da sanyin safiyar Larabar nan, inda bayan musayar wuta da masu tsaron ofishin, sai suka tada wasu bama bamai dake jikin su, wanda hakan ya sabbaba rasuwar mutane da dama, tare da jikkata wasu.

Wannan hari dai na zuwa ne, yayin da gwamnatin kasar mai samun goyon bayan MDD, ke hadin gwiwa da tawagar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya a kasar, wajen shirya zaben shugaban kasa da na 'yan majalissu, kafin nan da karshen wannan shekara ta bana, kamar da yadda shugaban tawagar, Ghassan Salame ya bada shawarar aiwatarwa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China