in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin ruwa na kasar Libya sun ceto bakin haure 120 daga yammacin bakin tekun kasar
2018-04-24 14:39:12 cri

Jiya Litinin, sojojin ruwa na kasar Libya sun ceto wasu bakin haure su 120 daga bakin tekun kasar daura da birnin Garrabulli, mai nisan kilomita kimamin 55 da Tripoli, babban birnin kasar.

Kwamandan sojojin ruwan Milad Abdalkarim ya zanta da wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin, inda ya bayyana cewa an ceci wadannan bakin haure ne 'yan kasashen Afirka daban daban daga tekun da ke da nisan mil 50 daga gabar birnin Garrabulli. Ya kuma kara da cewa, an riga an kai su sansanin sojojin ruwa na Tripoli.

Kakakin sojojin ruwan kasar ya bayyana a Lahadin da ta gabata cewa, an riga an samu gawawwakin wasu bakin hauren su 11, sa'an nan an ceto wasu 283 daga tekun kasar bisa matakai daban daban da aka dauka.

Bisa kididdigar da aka bayar, an ce, cikin watannin 3 na farkon wannan shekara, an riga an ceto bakin haure fiye da 400 daga bakin tekun kasar ta Libya.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China