in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta yi amfani da sakamakon taron kungiyar kawancen kasashen Larabawa da na Tarayyar Afrika wajen mara ga cikakken ikon kasar Libya
2018-04-20 10:36:18 cri
Shugaban shirin MDD dake aiki a Libya Ghassan Salame, ya ce shirin na duba yiwuwar amfani da sakamakon tarukan baya-bayan nan, na kawancen kasashen Larabawa da na kwamitin manyan jami'an Tarayyar Afrika game da Libya, ta yadda zai amfanawa cikakken ikon da kasar ke da shi.

Ghassan Salame ya bayyana haka ne jiya a birnin Tripoli, yayin wani taron manema labarai da ya biyo bayan ganawarsa da Mahamed Sayala, Ministan harkokin wajen Gwamnatin Libya da MDD ke marawa baya.

Ya kara da cewa, ya halarci tarukan tare da Mohamed Sayala, kuma sun tattauna kan yadda za a yi amfani da sakamakon tarukan domin amfanawa cikakken ikon mallakar kasa da 'yancin kan da Libya ke da shi.

A baya-bayan nan ne a ka gudanar da taron kasashen Larabawa a birnin Dhahran na Saudiyya, wanda ya samu halartar shugabannin yankin.

Har ila yau, an gudanar taron kwamitin Ministocin Tarayyar Afrika kwanaki biyu da suka wuce a birnin Addis Ababa na Ethiopia, inda ya bayyana goyon bayansa ga cikakken ikon da tsarin siyasar kasar bisa manufofin MDD, wanda ya dogara da gudanar da zaben kasar kafin karshen bana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China