in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Libya ta yi tir da mummunan harin aka kai Benghazi
2018-05-26 15:26:22 cri
Gwamnatin Libya da MDD ke marawa baya, ta yi tir da harin bam da aka kai cikin mota, a gabashin birnin Benghazi a jiya, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 6 tare da raunata wasu sama da 20.

Cikin wata sanarwa da ta fitar, Gwamnatin hadin kan kasar, ta yi Allah wadai da harin da aka kai titin Jamal Abdannaser na Benghazi a jiya Alhamis. Inda da ta ce babu abun da zai yi, face sa al'ummar kasar kara jajircewa wajen yaki da ta'addanci.

Ita ma Majalisar wakilan kasar dake da zama a yankin, ta yi tir da harin, ta na mai kira ga hukumomin tsaron kasar, su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu, na nemo wadanda ke da hannu tare da hukunta su.

Benghazi wanda shi ne birni na 2 mafi girma a Libya, ya sha fuskantar hare-haren cikin mota da kuma na kunar bakin wake.

A wani mataki na tunkarar tabarbarewar tsaro ne birnin ya kafa wata rundunar hadin gwiwa da ta kunshi sojoji da 'yan sanda.

A bara ne kuma, rundunar soji dake yankin, karkashin Janar Khalifa Haftar, ta samu damar kwace iko da Benghazi, bayan shafe sama da shekaru 3 ta na gwabzawa da kungiyoyin 'yan ta'adda a birnin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China