in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rahoton IAEA ya nuna yadda Iran ke biyayya ga yarjejeniyar nukiliyar ta
2018-05-25 09:59:55 cri
Wani rahoton hukumar dake lura da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA, ya nuna cewa kasar Iran na ci gaba da biyayya ga yarjejeniyar nukiliyarta da aka cimma, duk da ficewar da Amurka ta yi daga yarjejeniyar.

Kamfanin dillancin labarai na Xinhua, wanda ya samu ganin kwafin rahoton ya bayyana cewa, IAEA na sanya ido ga tsare tsaren kasar Iran, game da ayyukan ta na sarrafa makamashin nukiliya ko JCPOA takaice. Kuma ba wasu alamu na zahiri, dake nuna cewa kasar ta karya yarjejeniyar.

Rahoton ya kara da cewa, Tehran na kiyaye dukkanin ayyuka da suka jibanci sarrafa ruwan sinadarai, da makamashi, da wuraren binciken sarrafa sinadaran nukiliya da dai sauran su, wadanda duka bangarori ne na waccan yarjejeniya.

Wakilan kasashen Sin da Rasha, da Birtaniya, da Faransa, da Jamus da Iran, za su gana a yau Juma'a a birnin Vienna, domin tattauna makomar yarjejeniyar da aka kulla, a zaman da zai kasance na farko tun bayan ficewar Amurka.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China