Merkel wadda ta bayyana hakan Jumma'ar nan a birnin Muenster dake yammacin kasar Jamus, ta ce hakan ta kawo illa ga dokokin kasa da kasa ne. Ta ce koda yake ba a kai ga aiwatar da yarjejeniyar ba kuma har yanzu ba a warware wasu batutuwa ba, amma duk da haka janyewar Amurka daga wannan yarejejniya abin damuwa ne da takaici. (Ibrahim)