in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan Koriya ta arewa da Amurka za su dauki matakan tabbatar da nasarar ganawar shugabanninsu
2018-05-16 19:26:33 cri
Mahukuntan kasar Sin, sun bayyana fatan ganin Koriya ta arewa, da Amurka, za su dauki matakan tabbatar da nasarar ganawar shugabannin kasashen biyu kamar yadda aka tsara.

Sin dai na fatan hakan zai ba da wata kafa, ta cimma nasarar kawo karshen makaman nukiliya a zirin Koriya, tare da wanzar da zaman lafiya da lumana a zirin.

Wata kafar watsa labaran Koriya ta arewa (DPRK) ta bayyana a Larabar nan cewa, Pyongyang ta dage aniyar tattaunawar manyan jami'ai tare da Koriya ta kudu, kana mai yiyuwa ne za ta janye daga tattaunawar da aka tsara gudanarwa da tsagin Amurka, sakamakon atisayen soji na hadin gwiwa da Amurka ke gudanarwa tare da Koriya ta kudu a halin yanzu. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China