in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi maraba da sanarwar hadin gwiwar da DPRK da ROK suka cimma
2018-04-27 20:15:23 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya ce, kasarsa ta yi maraba da sanarwar hadin gwiwa da kasashen Koriya ta kudu da ta Arewa suka cimma, tana mai bayyana fatan sassan biyu za su aiwatar da matsayar taron kolin da suka cimma domin ganin an kai ga sassantawa da yin hadin gwiwa.

Lu Kang wanda ya sanar da hakan yayin taron manema labarai a yau Jumma'a, ya ce shugabannin biyu sun kuma tabbatar da matsaya daya game da kawar da nukiliya a yankin. Bugu da kari sun amince su ci gaba da yin tattaunawa wajen ganin an cimma yarjejeniyar zaman lafiya, bayan ganawar farko da shugabannin biyu suka yi a yau Jumma'a a kauyen Panmunjom.

Madam Hua ta kara da dewa, shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa da takwaransa Moon Jae-in na Koriya ta Kudu, sun kuma sanya hannu a kan sanarwar hadin gwiwar, mai taken "sanarwar zaman lafiya da hadewar zirin Koriya ta Panmunjom" wanda ya gudana a gidan zaman lafiya dake yankin Koriya ta kudu, kusa da kauyen da aka sanya hannu kan yarjejeniyar kawo karshen yakin kasashen biyu a shekarar 1953. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China