in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yaba karfin halin da shugabannin DPRK da ROK suna nuna
2018-04-27 19:22:34 cri
Kasar Sin ta yaba da matakin siyasa da ma karfin halin da shugabanin kasashen Koriya ta Kudu da na Arewa suka nuna tare da yi musu fatan samun sakamako mai kyau a ganawarsu.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying wadda ta bayyana hakan Jumma'ar nan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa a nan birnin Beijing, ta ce duniya ta kalli yadda shugabannin kasashen biyu suka yi ganawar tarihi a yankin da ya raba kasashen biyu ta kafar talabijin, kuma kasar Sin ta yaba da wannan jarumta da shugabannin suka nuna.

Ta ce shugaba Moon Jae-in ta Koriya ta Kudu da takwaransa na Koriya ta Arewa Kim Jong Un, sun tabbatar da buri guda na kawar da makaman nukiliya a yankin. Sun kuma amince su ci gaba da tattaunawa da za ta kai ga cimma yarjejeniyar zaman lafiya, bayan ganawarsu ta farko a kan iyakar kauyen Panmunjom a yau Jumma. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China