in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yabawa aniyar Koriya ta arewa ta rushe wurin gwajin makaman nukiliya
2018-05-14 20:41:56 cri
Kasar Sin ta yabawa aniyar Koriya ta arewa, game da rushe wurin gwajin makamanta na nukiliya, wanda aka tsara gudanarwa tsakanin ranekun 23 zuwa 25 ga watan nan na Mayu.

Da yake bayyana hakan yayin taron manema labarai a Litinin din nan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Lu Kang ya ce matakin na Koriya ta arewa ya nuna kyakkyawar aniyarta, ta kawo karshen makaman nukiliya a zirin koriya, tare da karfafa amincewa da juna tsakanin kasashe masu ruwa da tsaki a batun nukiliyar kasar.

Jami'in na Sin, ya ce hakan wani mataki ne da ya dace da burin da aka sanya gaba, game da warware batun makaman nukiliya a zirin koriya ta hanyar lumana, wanda kuma ya dace dukkanin sassa su ba shi goyon baya da tallafin da ya kamata. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China