in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na kokarin sanya takunkumi ga masu kokarin kawo zagon kasa a Sudan ta kudu
2018-04-26 20:22:11 cri
Shugaban hukumar zartarswar kungiyar tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, ya ce kungiyar tana duba yiwuwar kakabawa shugabannin dake kokarin yin zagon kasa ga shirin wanzar da zaman lafiyar kasar Sudan ta kudu.

Shugaban wanda ya bayyana hakan a yau Alhamis yayin da yake tattaunawa da shugaba Uhuru Kenyatta na Kenya a birnin Nairobin kasar Kenya, ya yaba da kokarin Kenya na samar da zaman lafiya a shiyyar kana ya yi kira ga kasashen dake shiyyar, da su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a Sudan ta kudun.

Mahamat ya kuma yi kira ga shugaba Kenyatta da takwarorinsu na gabashin Afirka da su ci gaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Sudan ta kudu. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China