in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasa da kasa suna hada kai wajen yaki da yaduwar cutar Ebola a DRC
2018-05-27 16:44:25 cri
A ranar 8 ga wannan wata, an tabbatar da barkewar cutar Ebola a kasar Congo Kinshasa DRC. Bisa kididdigar da hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO ta bayar, an ce, ya zuwa ranar 24 ga wannan wata, an gabatar da mutane 54 da ake zargin sun kamu cutar Ebola, an tabbatar mutane 35 daga cikinsu sun kamu da cutar, kuma yawan mutuwar mutanen a sakamakon cutar ya kai 23. Idan aka kwatanta wannan hali bisa na lokacin baya a yankin Afirka, ana iya dakile bazuwar cutar da saurin yaduwarta a wannan kasa, an samu nasarar hakan ne a sakamakon hadin gwiwar kasa da kasa da suka dauki matakai cikin gaggawa.

Bayan da aka tabbatar da barkewar cutar Ebolar, hukumar WHO, da asusun tallafawa kananan raya na MDD, da kungiyar AU da sauran hukumomin duniya, da kasar Sin, da kasar Guinea, da sauran kasashen duniya, sun dauki matakai nan da nan don magance yaduwar cutar Ebola kamar yadda aka yi a lokacin yaduwar cutar Ebola a shekarar 2014 zuwa 2016.

Kungiyar AU ta sanar da cewa, cibiyar hana yaduwar cututtuka ta Afirka dake karkashin jagorancinta, ta kaddamar da shirin tinkarar batun cikin gaggawa, da nuna goyon baya ga kasar Congo Kinshasa wajen yaki da kuma magance cutar Ebola, da tura rukunin jami'an ba da jinya da rigakafin cutar Ebolar zuwa kasar Congo Kinshasa.

A kwanakin baya, direktan kwamitin kiwon lafiya na kasar Sin dake halartar taron kiwon lafiya na duniya da aka gudanar a birnin Geneva Ma Xiaowei, ya bayyana cewa, Sin ta dora muhimmanci sosai ga halin cutar Ebola da ta barke a kasar Congo Kinshasa, da samar da gudummawa da tura rukunin likitoci zuwa kasar Congo Kinshasa da zarar an bukaci hakan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China