in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta yi jan hankali game da barkewar Ebola a DR Congo
2018-05-13 15:21:02 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO ta yi gargadin cewa, dakile yaduwar cutar Ebola a janhuriyar dimokaradiyyar Congo, zai zamo wani jan aiki mai tattare da kalubale, wanda kuma zai bukaci tarin kudade, da shiri na musamman na fuskantar abun da ka je ya zo.

Babban daraktan WHO Dr. Tedros Adhanom Ghebreyesus, na shirin ziyartar kasar cikin karshen makon nan, domin duba halin da ake ciki, ya kuma bada umarnin ci gaba da gudanar da ayyukan jin kai, karkashin tsare tsaren kiwon lafiyar da hukumomin kasar ke aiwatarwa.

Wasu alkaluma sun nuna cewa, ya zuwa ranar Juma'a, yawan wadanda ake zaton sun kamu da cutar Ebola a kasar a tsakanin makwanni 5 sun kai mutum 34, ciki hadda mutum 2 da aka tabbatar suna dauke da cutar, da 18 da suka riga suka rasu ake kuma zaton cutar ce ta hallaka su, sai kuma wasu 14 da ba a riga an tabbatar da kamuwar su ba tukuna.

Kaza lika an dauki jinin wasu mutanen 5, inda aka samu 2 daga cikin su na dauke da cutar ta Ebol, a bayan gudanar da gwaje gwaje a dakin bincike. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China