in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO za ta yi gwajin allurar rigakafin cutar Ebola a DRC
2018-05-15 10:03:11 cri
Babban direktan hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana a birnin Kinshasa na kasar Congo Kinshasa DRC a kwanakin baya cewa, hukumar tana shirin gwajin allurar rigakafin cutar Ebola a yankin arewa maso yammacin kasar. Gobe Laraba ko Alhamis ne ake sa ran isowar alluran.

Alkaluman kididdigar hukumar WHO na nuna cewa, daga ranar 4 ga watan Afrilu zuwa 13 ga watan Mayu, an samu rahoton mutane 39 da aka tabbatar ko ake zargin sun kamu da cutar Ebola, a kalla mutane 18 daga cikinsu sun mutu.

Yankin da cutar ta barke a wannan karo wato yankin Bikoro dake jihar Equateur yana kusa da arewa maso yammacin iyakar kasar.

Wannan ne karo na 9 da aka samu bullar cutar Ebola tun bayan da aka fara gano cutar a kasar Congo Kinshasa a shekarar 1976 a karon farko. Hukumar WHO ta ayyana kasar da kasashen dake kewayenta a matsayin matsakaicin kasashe masu tinkarar kalubalen cutar Ebola, da yin hadin gwiwa tare da kasashen wajen sa ido kan cutar da shirya tinkarar hadarin bazuwar cutar tare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China