in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta inganta matakan tunkarar yuwuwar barkewar Cutar Ebola
2018-05-11 10:02:20 cri
Ministan lafiya na Nijeriya, Isaac Adewole, ya ce, tun bayan barkewar cutar Ebola a shekarar 2014, lokacin da wani BaAmurke kuma dan Liberia, Patrick Sawyer ya kai cutar kasar, ba a daina binciken fasinjojin dake shiga kasar ba a filayen jirgin sama.

A ranar Laraba ne majalisar zartarwar kasar, ta umarci ma'aikatar lafiyar da ta inganta matakan sa ido, domin tunkarar yuwuwar barkewar Ebola a kasar.

Da yake ganawa da manema labarai jiya, a Abuja babban birnin kasar, Isaac Adewole, ya ce umarnin na majalisar zartarwar, ya biyo bayan rahoton barkewar cutar a Jamhuriyar Demokradioyyar Congo.

A nata bangaren, Kakakin hukumar kula da filayen jiragen saman kasar (FAAN) Henrietta Yakubu, ta shaidawa Xinhua cewa, har yanzu, hukumar na da kayakin aiki da isassun jami'ai a filayen jirgin sama domin kare cutar daga shiga kasar. Ta ce hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba, a kokarin da take na tabbatar da binciken dukkan fasinjoji masu shiga kasar yadda ya kamata a filayen jirgen sama. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China