in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu sharhi: Karar da wasu 'yan gudun hijirar Najeriya suka shigar kan kasar Italiya zai zama aya ga wasu
2018-05-14 09:37:18 cri
Wasu masharhanta sun bayyana cewa, karar da wasu gungun 'yan gudun hijirar Najeriya suka shigar kan yadda kasar Italiya ta sanya rayuwarsu cikin hadari da keta 'yancinsu na bil-Adama, ta hanyar goyon baya da taimakawa jami'an jiragen ruwan Libya, shi ne irinsa na farko, kuma zai zama izna ga masu aikata irin haka a nan gaba.

Wannan kara dai ta sha banbam da saura, saboda tana neman kasar Italiya ta biya diyya kan matakan da kasar Libya ta dauka, dangane da zargin da ake mata na keta 'yancin bil-Adama.

Su dai 'yan Najeriyar sun tsira ne a kokarin da suke na tsallakawa kasar Italiya a shekarar da ta gabata, tafiyar da suka ce na cike da hadari sakamakon tsauraran manufofin Libya masu cike da hadari da kasar ta dauka na kokarin tilastawa 'yan gudun hijira da jiragen ruwan dake dauke da bakin haure komawa yankin ruwan Afirka

Wannan manufa dai wani bangare ne na kokarin da mahukuntan kasar Italiya ke yi na hana bakin haure daga kasashe matalauta da wadanda ke fama da yake-yake a Afirka da yankin gabas ta tsakiya shiga kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China