in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana taka rawa wajen tafiyar da harkokin kiwon lafiya na kasa da kasa
2018-05-21 10:31:18 cri
Wani babban jami'in kiwon lafiya na kasar Sin ya bayyana cewa, kiwon lafiya jigo ne wajen cimma nasarar ajandar dawwamamman ci gaba nan da shekarar 2030, kana kasar Sin ta tsaya tsayin daka wajen tafiyar da harkokin kiwon lafiya na kasa da kasa.

Ma Xiaowei, shugaban kwamitin lafiyar kasar Sin, kana jagoran tawagar kasar Sin mahalarta taron kiwon lafiya na duniya karo na 71 (WHA) wanda za'a bude a Geneva a ranar Litinin.

Ya bayyana a lokacin taron manema labarai a jiya Lahadi cewa, kasar Sin tana bada muhimmanci matuka wajen ceto lafiyar al'ummar kasarta, da inganta jin dadin rayuwar al'ummarta, kana kasar Sin tana taka rawa wajen tafiyar da harkokin kiwon lafiya na kasa da kasa.

A matsayinta na babbar kasa mai tasowa a duniya, kasar Sin ta samu nasarori masu tarin yawa a fagen tafiyar da harkokin kiwon lafiya kuma a shirye take ta yi musayar kwarewar da ta samu da sauran kasashen duniya, in ji mista Ma.

Ya ce a ayyukan da take yi tare da cibiyoyin bincike a Afrika, kasar Sin ta kaddamar da wasu ayyuka domin Afrika ta koya don amfanin al'umomin kasashen a bangaren rigakafi da magance cutar zazzabin malaria da dangoginsa, ya kara da cewa, kasar Sin ita ce ta farko a duniya wajen kaddamar da shirin kai daukin gaggawa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China